Ishaya 38:1-21 HAUCB2020 - Bible AI

1A kwanakin nan sai Hezekiya ya kamu da ciwo ya kuma kusa ya mutu. Annabi Ishaya ɗan Amoz ya tafi wurinsa ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji* ya ce ka shirya gidanka, domin za ka mutu; ba za ka warke ba.”

2Hezekiya ya juye fuskarsa wajen bango ya kuma yi addu’a ga Ubangiji*,

3“Ka tuna, ya Ubangiji*, yadda na yi tafiya a gabanka da aminci da dukan zuciya na kuma yi abin da yake nagari a idanunka.” Sai Hezekiya ya yi kuka mai zafi.

4Sai maganar Ubangiji* ta zo wa Ishaya cewa,

5“Ka tafi ka faɗa wa Hezekiya, ‘Ga abin da Ubangiji* Allah na kakanka Dawuda, ya ce na ji addu’arka na kuma ga hawayenka; zan ƙara maka shekaru goma sha biyar ga rayuwarka.

6Zan kuwa cece ka da wannan birni daga hannun sarkin Assuriya. Zan kiyaye wannan birni.

7“ ‘Ga alamar Ubangiji* gare ka cewa Ubangiji* zai aikata kamar yadda ya yi alkawari.

8Zan sa inuwar da rana ta yi a kan matakalar Ahaz ta koma baya da taki goma.’ ” Saboda haka inuwar ta koma da baya daga fuskar rana har taki goma.

9Rubutun Hezekiya sarkin Yahuda bayan ciwonsa da kuma warkarwarsa.

10Na ce, “Cikin tsakiyar rayuwata

11Na ce, “Ba zan ƙara ganin Ubangiji* ba,

12Kamar tentin makiyayi

13Na yi jira da haƙuri har safiya,

14Na yi kuka kamar mashirare ko zalɓe,

15Amma me zan ce?

16Ubangiji, ta waɗannan abubuwa ne mutane suke rayuwa;

17Tabbatacce wannan kuwa saboda ribata ne

18Gama kabari ba zai yabe ka ba,

19Masu rai, masu rai, su suke yabonka,

20Ubangiji* zai cece ni,

21Ishaya ya riga ya ce, “Ku shirya curin da aka yi da ’ya’yan ɓaure ku kuma shafa a marurun, zai kuwa warke.”

>