1Mala’ikan Ubangiji* ya haura daga Gilgal zuwa Bokim ya ce, “Na hauro da ku daga Masar zuwa ƙasar da na rantse zan ba wa kakanninku. Na ce, ‘Ba zan taɓa tā da yarjejjeniyata da ku ba,
2ku kuma kada ku shiga wata yarjejjeniya da mazaunan ƙasan nan, sai dai za ku rurrushe bagadansu.’ Duk da haka ba ku yi biyayya mini ba. Me ya sa kuka yi haka?
3Saboda haka ina gaya muku cewa ba zan kore su a gabanku ba; za su zama muku ƙaya, gumakansu kuma za su zama muku tarko.”
4Da mala’ikan Ubangiji* ya faɗa wa dukan Isra’ilawa waɗannan abubuwa, sai mutane suka yi kuka mai zafi,
5sai suka sa wa wannan wuri suna, Bokim.+ 2:5 Bokim yana nufin masu kuka.* A nan suka miƙa hadaya a gaban Ubangiji*.
6Bayan Yoshuwa ya sallami Isra’ilawa, sai suka tafi don su mallaki ƙasar, kowa da nasa gādon.
7Mutane suka bauta wa Ubangiji* duk tsawon kwanakin Yoshuwa da na dattawan da suka rayu bayansa waɗanda suka ga manyan abubuwan da Ubangiji* ya yi wa Isra’ila.
8Yoshuwa ɗan Nun, bawan Ubangiji*, ya mutu yana da shekara ɗari da goma.
9Aka binne shi a ƙasar gādonsa, a Timnat Heres+ 2:9 An kuma santa kamar Timnat Sera (dubi Yosh 19.50da Yosh 24.30).* a ƙasar tudu ta Efraim, arewa da Dutsen Ga’ash.
10Bayan tsaran nan duka suka rasu, sai wata tsara ta taso wadda ba tă san Ubangiji* ko abin da ya yi wa Isra’ila ba.
11Sai Isra’ilawa suka yi mugaye abubuwa a gaban Ubangiji* suka kuma bauta Ba’al.
12Suka yashe Ubangiji* Allah na kakanninsu, wanda ya fitar da su daga Masar. Suka bi suka kuma bauta alloli dabam-dabam na mutanen da suke kewaye da su. Suka tsokani Ubangiji* ya yi fushi
13domin sun bar shi suka bauta wa Ba’al da Ashtarot.
14Cikin fushinsa a kan Isra’ila Ubangiji* ya ba da su ga hannun waɗanda suka kawo musu hari suka washe su. Ya sayar da su ga abokan gābansu da suke kewaye da su, waɗanda ba za su iya yin tsayayya da su ba.
15Duk sa’ad da Isra’ila suka fita yaƙi, Ubangiji* yakan yi gāba da su don a ci su a yaƙi, kamar dai yadda ya rantse musu. Suka kuwa shiga wahala ƙwarai.
16Sa’an nan Ubangiji* ya naɗa mahukunta,+ 2:16 Ko kuwa shugabanni; daidai kamar a ayoyi 17-19.* waɗanda suka cece su daga hannun waɗannan musu hari.
17Duk da haka ba su saurari mahukuntansu ba amma sai suka shiga ha’inci da waɗansu alloli suka kuma bauta musu. Ba kamar kakanninsu ba, nan da nan suka kauce daga hanyar da kakanninsu suka bi, hanyar biyayya ga umarnan Ubangiji*.
18Duk sa’ad da Ubangiji* ya naɗa musu mahukunci, yakan kasance tare da mahukuncin, yă kuma cece su daga hannun abokan gāba, muddin mahukuncin yana a raye; gama Ubangiji* yakan ji tausayinsu yayinda suke gunaguni ƙarƙashin waɗanda suka danne su suke kuma gasa musu azaba.
19Amma sa’ad da mahukuncin ya mutu, mutanen suka koma hanyar da ta fi ta kakanninsu muni, sukan bi waɗansu alloli suna bauta musu. Suka ƙi barin mugun ayyukansu da taurin zuciyarsu.
20Saboda haka sai Ubangiji* ya fusata da Isra’ila ya ce, “Domin wannan al’umma ta tā da yarjejjeniyar da na yi da kakanninsu ba su kuwa saurare ni ba,
21ba zan ƙara kori wata al’ummar da Yoshuwa ya bari sa’ad da ya rasu ba.
22Zan yi amfani da su in gwada Isra’ila in ga ko za su bi hanyar Ubangiji* su kuma yi tafiya a cikinta kamar yadda kakanninsu suka yi.”