1Zan yabe ka, ya Ubangiji*, da dukan zuciyata;
2Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikinka;
3Abokan gābana sun ja da baya;
4Gama ka tabbata da gaskiyata da kuma abin da nake yi;
5Ka tsawata wa ƙasashe ka kuma hallakar da mugaye;
6Lalaci marar ƙarewa ya cimma abokan gābanmu,
7Ubangiji* yana mulki har abada;
8Zai hukunta duniya da adalci;
9Ubangiji* shi ne mafakan waɗanda ake danniya,
10Waɗanda suka san sunanka za su dogara da kai,
11Rera yabai ga Ubangiji*, wanda yake zaune a kursiyi a Sihiyona;
12Gama shi da yakan ɗauki fansa a kan mai kisa yakan tuna;
13Ya Ubangiji*, dubi yadda abokan gābana suna tsananta mini!
14don in furta yabanka
15Al’umma sun fāɗa cikin ramin da suka haƙa wa waɗansu;
16An san Ubangiji* ta wurin gaskiyarsa;
17Mugaye za su koma kabari,
18Amma har abada ba za a manta da mai bukata ba,
19Ka tashi, ya Ubangiji*, kada ka bar wani yă yi nasara;